Hausa
Surah Al-Ghashiya ( The Overwhelming ) - Aya count 26
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ الْغَاشِيَةِ
( 1 ) 
Lalle ne labãrin (¡iyãma) mai rufe mutãne da tsoronta yã zo maka?
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ خَاشِعَةٌ
( 2 ) 
Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.
عَامِلَةٌ نَّاصِبَةٌ
( 3 ) 
Mãsu aikin wahala ne, mãsu gajiya.
تَصْلَىٰ نَارًا حَامِيَةً
( 4 ) 
Zã su shiga wata wuta mai zãfi.
تُسْقَىٰ مِنْ عَيْنٍ آنِيَةٍ
( 5 ) 
Ana shãyar da su daga wani marmaro mai zãfin ruwa.
لَّيْسَ لَهُمْ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٍ
( 6 ) 
Ba su da wani abinci fãce dai daga danyi.
لَّا يُسْمِنُ وَلَا يُغْنِي مِن جُوعٍ
( 7 ) 
Bã ya sanya ƙiba, kuma bã zai wadãtar daga yunwa ba.
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاعِمَةٌ
( 8 ) 
Wasu huskõki a rãnar nan mãsu ni'ima ne.
لِّسَعْيِهَا رَاضِيَةٌ
( 9 ) 
Game da aikinsu, masu yarda ne.
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍ
( 10 ) 
(Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya.
لَّا تَسْمَعُ فِيهَا لَاغِيَةً
( 11 ) 
Bã zã su ji yãsassar magana ba, a cikinta.
فِيهَا عَيْنٌ جَارِيَةٌ
( 12 ) 
A cikinta akwai marmaro mai gudãna.
فِيهَا سُرُرٌ مَّرْفُوعَةٌ
( 13 ) 
A cikinta akwai gadãje maɗaukaka.
وَأَكْوَابٌ مَّوْضُوعَةٌ
( 14 ) 
Da kõfuna ar'aje.
وَنَمَارِقُ مَصْفُوفَةٌ
( 15 ) 
Da filõli jẽre,
وَزَرَابِيُّ مَبْثُوثَةٌ
( 16 ) 
Da katifu shimfiɗe.
أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى الْإِبِلِ كَيْفَ خُلِقَتْ
( 17 ) 
Ashe to bã zã su dũbãwa ba ga rãƙumã yadda aka halitta su?
وَإِلَى السَّمَاءِ كَيْفَ رُفِعَتْ
( 18 ) 
Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta?
وَإِلَى الْجِبَالِ كَيْفَ نُصِبَتْ
( 19 ) 
Da zuwa ga duwãtsu yadda aka kafa su?
وَإِلَى الْأَرْضِ كَيْفَ سُطِحَتْ
( 20 ) 
Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗã ta?
فَذَكِّرْ إِنَّمَا أَنتَ مُذَكِّرٌ
( 21 ) 
sabõda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.
لَّسْتَ عَلَيْهِم بِمُصَيْطِرٍ
( 22 ) 
Ba ka zama mai ĩkon tanƙwasãwa a kansu ba.
إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ
( 23 ) 
Fãce dai duk wanda ya jũya bãya, kuma ya kãfirta.
فَيُعَذِّبُهُ اللَّهُ الْعَذَابَ الْأَكْبَرَ
( 24 ) 
To, Allah zai yi masa azãba, azãbar nan da take mafi girma.
إِنَّ إِلَيْنَا إِيَابَهُمْ
( 25 ) 
Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take.
ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا حِسَابَهُم
( 26 ) 
Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi.