Surah An-Nazi'at ( Those who Pull Out )

Select reciter

Hausa

Surah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya count 46
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email
وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًا ( 1 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 1
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًا ( 2 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 2
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًا ( 3 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 3
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًا ( 4 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 4
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًا ( 5 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 5
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُ ( 6 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 6
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُ ( 7 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 7
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ ( 8 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 8
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌ ( 9 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 9
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
يَقُولُونَ أَإِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِ ( 10 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 10
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
أَإِذَا كُنَّا عِظَامًا نَّخِرَةً ( 11 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 11
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ ( 12 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 12
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ ( 13 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 13
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
فَإِذَا هُم بِالسَّاهِرَةِ ( 14 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 14
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ ( 15 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 15
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًى ( 16 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 16
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
اذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىٰ ( 17 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 17
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰ أَن تَزَكَّىٰ ( 18 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 18
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ ( 19 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 19
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَاهُ الْآيَةَ الْكُبْرَىٰ ( 20 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 20
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ( 21 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 21
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ ( 22 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 22
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ( 23 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 23
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الْأَعْلَىٰ ( 24 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 24
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الْآخِرَةِ وَالْأُولَىٰ ( 25 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 25
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰ ( 26 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 26
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
أَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاءُ ۚ بَنَاهَا ( 27 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 27
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَا ( 28 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 28
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَا ( 29 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 29
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
وَالْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَاهَا ( 30 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 30
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَا ( 31 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 31
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَا ( 32 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 32
Da duwatsu, Yã kafe ta.
مَتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ ( 33 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 33
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ ( 34 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 34
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ مَا سَعَىٰ ( 35 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 35
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ ( 36 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 36
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ ( 37 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 37
To, amma wanda ya yi girman kai.
وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا ( 38 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 38
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىٰ ( 39 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 39
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىٰ ( 40 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 40
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىٰ ( 41 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 41
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَا ( 42 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 42
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَاهَا ( 43 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 43
Me ya haɗã ka da ambatonta?
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَاهَا ( 44 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 44
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَاهَا ( 45 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 45
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَا ( 46 ) An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) - Aya 46
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email

Select language

Select surah