Surah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter )

Select reciter

Hausa

Surah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya count 60
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email
وَالذَّارِيَاتِ ذَرْوًا ( 1 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 1
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
فَالْحَامِلَاتِ وِقْرًا ( 2 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 2
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
فَالْجَارِيَاتِ يُسْرًا ( 3 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 3
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
فَالْمُقَسِّمَاتِ أَمْرًا ( 4 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 4
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٌ ( 5 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 5
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
وَإِنَّ الدِّينَ لَوَاقِعٌ ( 6 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 6
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الْحُبُكِ ( 7 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 7
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
إِنَّكُمْ لَفِي قَوْلٍ مُّخْتَلِفٍ ( 8 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 8
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
يُؤْفَكُ عَنْهُ مَنْ أُفِكَ ( 9 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 9
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
قُتِلَ الْخَرَّاصُونَ ( 10 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 10
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
الَّذِينَ هُمْ فِي غَمْرَةٍ سَاهُونَ ( 11 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 11
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
يَسْأَلُونَ أَيَّانَ يَوْمُ الدِّينِ ( 12 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 12
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
يَوْمَ هُمْ عَلَى النَّارِ يُفْتَنُونَ ( 13 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 13
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
ذُوقُوا فِتْنَتَكُمْ هَٰذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تَسْتَعْجِلُونَ ( 14 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 14
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ ( 15 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 15
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
آخِذِينَ مَا آتَاهُمْ رَبُّهُمْ ۚ إِنَّهُمْ كَانُوا قَبْلَ ذَٰلِكَ مُحْسِنِينَ ( 16 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 16
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
كَانُوا قَلِيلًا مِّنَ اللَّيْلِ مَا يَهْجَعُونَ ( 17 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 17
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
وَبِالْأَسْحَارِ هُمْ يَسْتَغْفِرُونَ ( 18 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 18
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
وَفِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِ ( 19 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 19
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
وَفِي الْأَرْضِ آيَاتٌ لِّلْمُوقِنِينَ ( 20 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 20
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
وَفِي أَنفُسِكُمْ ۚ أَفَلَا تُبْصِرُونَ ( 21 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 21
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
وَفِي السَّمَاءِ رِزْقُكُمْ وَمَا تُوعَدُونَ ( 22 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 22
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
فَوَرَبِّ السَّمَاءِ وَالْأَرْضِ إِنَّهُ لَحَقٌّ مِّثْلَ مَا أَنَّكُمْ تَنطِقُونَ ( 23 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 23
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ ضَيْفِ إِبْرَاهِيمَ الْمُكْرَمِينَ ( 24 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 24
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
إِذْ دَخَلُوا عَلَيْهِ فَقَالُوا سَلَامًا ۖ قَالَ سَلَامٌ قَوْمٌ مُّنكَرُونَ ( 25 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 25
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
فَرَاغَ إِلَىٰ أَهْلِهِ فَجَاءَ بِعِجْلٍ سَمِينٍ ( 26 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 26
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,
فَقَرَّبَهُ إِلَيْهِمْ قَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ ( 27 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 27
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
فَأَوْجَسَ مِنْهُمْ خِيفَةً ۖ قَالُوا لَا تَخَفْ ۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَامٍ عَلِيمٍ ( 28 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 28
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
فَأَقْبَلَتِ امْرَأَتُهُ فِي صَرَّةٍ فَصَكَّتْ وَجْهَهَا وَقَالَتْ عَجُوزٌ عَقِيمٌ ( 29 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 29
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
قَالُوا كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِ ۖ إِنَّهُ هُوَ الْحَكِيمُ الْعَلِيمُ ( 30 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 30
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا الْمُرْسَلُونَ ( 31 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 31
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"
قَالُوا إِنَّا أُرْسِلْنَا إِلَىٰ قَوْمٍ مُّجْرِمِينَ ( 32 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 32
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن طِينٍ ( 33 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 33
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَ ( 34 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 34
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ الْمُؤْمِنِينَ ( 35 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 35
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍ مِّنَ الْمُسْلِمِينَ ( 36 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 36
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
وَتَرَكْنَا فِيهَا آيَةً لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ الْعَذَابَ الْأَلِيمَ ( 37 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 37
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
وَفِي مُوسَىٰ إِذْ أَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍ ( 38 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 38
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.
فَتَوَلَّىٰ بِرُكْنِهِ وَقَالَ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ ( 39 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 39
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
فَأَخَذْنَاهُ وَجُنُودَهُ فَنَبَذْنَاهُمْ فِي الْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌ ( 40 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 40
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
وَفِي عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ الرِّيحَ الْعَقِيمَ ( 41 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 41
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
مَا تَذَرُ مِن شَيْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلَّا جَعَلَتْهُ كَالرَّمِيمِ ( 42 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 42
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
وَفِي ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا حَتَّىٰ حِينٍ ( 43 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 43
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
فَعَتَوْا عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ الصَّاعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَ ( 44 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 44
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
فَمَا اسْتَطَاعُوا مِن قِيَامٍ وَمَا كَانُوا مُنتَصِرِينَ ( 45 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 45
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا قَوْمًا فَاسِقِينَ ( 46 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 46
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
وَالسَّمَاءَ بَنَيْنَاهَا بِأَيْدٍ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ ( 47 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 47
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
وَالْأَرْضَ فَرَشْنَاهَا فَنِعْمَ الْمَاهِدُونَ ( 48 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 48
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
وَمِن كُلِّ شَيْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ ( 49 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 49
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
فَفِرُّوا إِلَى اللَّهِ ۖ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ ( 50 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 50
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
وَلَا تَجْعَلُوا مَعَ اللَّهِ إِلَٰهًا آخَرَ ۖ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ ( 51 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 51
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
كَذَٰلِكَ مَا أَتَى الَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُوا سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ ( 52 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 52
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
أَتَوَاصَوْا بِهِ ۚ بَلْ هُمْ قَوْمٌ طَاغُونَ ( 53 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 53
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَا أَنتَ بِمَلُومٍ ( 54 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 54
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
وَذَكِّرْ فَإِنَّ الذِّكْرَىٰ تَنفَعُ الْمُؤْمِنِينَ ( 55 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 55
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ ( 56 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 56
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
مَا أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍ وَمَا أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِ ( 57 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 57
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
إِنَّ اللَّهَ هُوَ الرَّزَّاقُ ذُو الْقُوَّةِ الْمَتِينُ ( 58 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 58
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا ذَنُوبًا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَابِهِمْ فَلَا يَسْتَعْجِلُونِ ( 59 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 59
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
فَوَيْلٌ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا مِن يَوْمِهِمُ الَّذِي يُوعَدُونَ ( 60 ) Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 60
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email

Select language

Select surah