Surah Ash-Shuara ( The Poets )

Select reciter

Hausa

Surah Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya count 227
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email
طسم ( 1 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 1
¦. S̃. M̃.
تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ الْمُبِينِ ( 2 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 2
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
لَعَلَّكَ بَاخِعٌ نَّفْسَكَ أَلَّا يَكُونُوا مُؤْمِنِينَ ( 3 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 3
Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
إِن نَّشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِم مِّنَ السَّمَاءِ آيَةً فَظَلَّتْ أَعْنَاقُهُمْ لَهَا خَاضِعِينَ ( 4 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 4
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
وَمَا يَأْتِيهِم مِّن ذِكْرٍ مِّنَ الرَّحْمَٰنِ مُحْدَثٍ إِلَّا كَانُوا عَنْهُ مُعْرِضِينَ ( 5 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 5
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.
فَقَدْ كَذَّبُوا فَسَيَأْتِيهِمْ أَنبَاءُ مَا كَانُوا بِهِ يَسْتَهْزِئُونَ ( 6 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 6
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
أَوَلَمْ يَرَوْا إِلَى الْأَرْضِ كَمْ أَنبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍ كَرِيمٍ ( 7 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 7
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ( 8 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 8
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 9 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 9
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
وَإِذْ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰ أَنِ ائْتِ الْقَوْمَ الظَّالِمِينَ ( 10 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 10
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
قَوْمَ فِرْعَوْنَ ۚ أَلَا يَتَّقُونَ ( 11 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 11
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"
قَالَ رَبِّ إِنِّي أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ ( 12 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 12
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
وَيَضِيقُ صَدْرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرْسِلْ إِلَىٰ هَارُونَ ( 13 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 13
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
وَلَهُمْ عَلَيَّ ذَنبٌ فَأَخَافُ أَن يَقْتُلُونِ ( 14 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 14
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
قَالَ كَلَّا ۖ فَاذْهَبَا بِآيَاتِنَا ۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسْتَمِعُونَ ( 15 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 15
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولَا إِنَّا رَسُولُ رَبِّ الْعَالَمِينَ ( 16 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 16
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."
أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِي إِسْرَائِيلَ ( 17 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 17
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."
قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدًا وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَ ( 18 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 18
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ الَّتِي فَعَلْتَ وَأَنتَ مِنَ الْكَافِرِينَ ( 19 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 19
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"
قَالَ فَعَلْتُهَا إِذًا وَأَنَا مِنَ الضَّالِّينَ ( 20 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 20
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."
فَفَرَرْتُ مِنكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكْمًا وَجَعَلَنِي مِنَ الْمُرْسَلِينَ ( 21 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 21
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
وَتِلْكَ نِعْمَةٌ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنْ عَبَّدتَّ بَنِي إِسْرَائِيلَ ( 22 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 22
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."
قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ الْعَالَمِينَ ( 23 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 23
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
قَالَ رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ ( 24 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 24
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُ أَلَا تَسْتَمِعُونَ ( 25 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 25
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ ( 26 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 26
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ الَّذِي أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُونٌ ( 27 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 27
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
قَالَ رَبُّ الْمَشْرِقِ وَالْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُمْ تَعْقِلُونَ ( 28 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 28
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
قَالَ لَئِنِ اتَّخَذْتَ إِلَٰهًا غَيْرِي لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ الْمَسْجُونِينَ ( 29 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 29
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَيْءٍ مُّبِينٍ ( 30 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 30
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
قَالَ فَأْتِ بِهِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ ( 31 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 31
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."
فَأَلْقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعْبَانٌ مُّبِينٌ ( 32 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 32
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.
وَنَزَعَ يَدَهُ فَإِذَا هِيَ بَيْضَاءُ لِلنَّاظِرِينَ ( 33 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 33
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.
قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُ إِنَّ هَٰذَا لَسَاحِرٌ عَلِيمٌ ( 34 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 34
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
يُرِيدُ أَن يُخْرِجَكُم مِّنْ أَرْضِكُم بِسِحْرِهِ فَمَاذَا تَأْمُرُونَ ( 35 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 35
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"
قَالُوا أَرْجِهْ وَأَخَاهُ وَابْعَثْ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَ ( 36 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 36
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٍ ( 37 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 37
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
فَجُمِعَ السَّحَرَةُ لِمِيقَاتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ ( 38 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 38
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.
وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنتُم مُّجْتَمِعُونَ ( 39 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 39
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?
لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ السَّحَرَةَ إِن كَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ ( 40 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 40
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."
فَلَمَّا جَاءَ السَّحَرَةُ قَالُوا لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجْرًا إِن كُنَّا نَحْنُ الْغَالِبِينَ ( 41 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 41
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"
قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذًا لَّمِنَ الْمُقَرَّبِينَ ( 42 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 42
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."
قَالَ لَهُم مُّوسَىٰ أَلْقُوا مَا أَنتُم مُّلْقُونَ ( 43 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 43
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."
فَأَلْقَوْا حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ الْغَالِبُونَ ( 44 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 44
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
فَأَلْقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ ( 45 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 45
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.
فَأُلْقِيَ السَّحَرَةُ سَاجِدِينَ ( 46 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 46
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
قَالُوا آمَنَّا بِرَبِّ الْعَالَمِينَ ( 47 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 47
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
رَبِّ مُوسَىٰ وَهَارُونَ ( 48 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 48
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
قَالَ آمَنتُمْ لَهُ قَبْلَ أَنْ آذَنَ لَكُمْ ۖ إِنَّهُ لَكَبِيرُكُمُ الَّذِي عَلَّمَكُمُ السِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ ۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُم مِّنْ خِلَافٍ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ ( 49 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 49
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."
قَالُوا لَا ضَيْرَ ۖ إِنَّا إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ ( 50 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 50
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
إِنَّا نَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَايَانَا أَن كُنَّا أَوَّلَ الْمُؤْمِنِينَ ( 51 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 51
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."
وَأَوْحَيْنَا إِلَىٰ مُوسَىٰ أَنْ أَسْرِ بِعِبَادِي إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ ( 52 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 52
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne.
فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَ ( 53 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 53
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.
إِنَّ هَٰؤُلَاءِ لَشِرْذِمَةٌ قَلِيلُونَ ( 54 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 54
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَائِظُونَ ( 55 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 55
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَاذِرُونَ ( 56 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 56
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
فَأَخْرَجْنَاهُم مِّن جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ ( 57 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 57
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.
وَكُنُوزٍ وَمَقَامٍ كَرِيمٍ ( 58 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 58
Da taskõki da mazauni mai kyau.
كَذَٰلِكَ وَأَوْرَثْنَاهَا بَنِي إِسْرَائِيلَ ( 59 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 59
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.
فَأَتْبَعُوهُم مُّشْرِقِينَ ( 60 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 60
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
فَلَمَّا تَرَاءَى الْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَابُ مُوسَىٰ إِنَّا لَمُدْرَكُونَ ( 61 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 61
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
قَالَ كَلَّا ۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهْدِينِ ( 62 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 62
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
فَأَوْحَيْنَا إِلَىٰ مُوسَىٰ أَنِ اضْرِب بِّعَصَاكَ الْبَحْرَ ۖ فَانفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْقٍ كَالطَّوْدِ الْعَظِيمِ ( 63 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 63
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
وَأَزْلَفْنَا ثَمَّ الْآخَرِينَ ( 64 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 64
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
وَأَنجَيْنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُ أَجْمَعِينَ ( 65 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 65
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
ثُمَّ أَغْرَقْنَا الْآخَرِينَ ( 66 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 66
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ( 67 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 67
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 68 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 68
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
وَاتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَاهِيمَ ( 69 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 69
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَا تَعْبُدُونَ ( 70 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 70
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"
قَالُوا نَعْبُدُ أَصْنَامًا فَنَظَلُّ لَهَا عَاكِفِينَ ( 71 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 71
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَ ( 72 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 72
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
أَوْ يَنفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَ ( 73 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 73
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
قَالُوا بَلْ وَجَدْنَا آبَاءَنَا كَذَٰلِكَ يَفْعَلُونَ ( 74 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 74
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
قَالَ أَفَرَأَيْتُم مَّا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ ( 75 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 75
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
أَنتُمْ وَآبَاؤُكُمُ الْأَقْدَمُونَ ( 76 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 76
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"
فَإِنَّهُمْ عَدُوٌّ لِّي إِلَّا رَبَّ الْعَالَمِينَ ( 77 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 77
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."
الَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهْدِينِ ( 78 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 78
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
وَالَّذِي هُوَ يُطْعِمُنِي وَيَسْقِينِ ( 79 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 79
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِ ( 80 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 80
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
وَالَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحْيِينِ ( 81 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 81
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
وَالَّذِي أَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لِي خَطِيئَتِي يَوْمَ الدِّينِ ( 82 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 82
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."
رَبِّ هَبْ لِي حُكْمًا وَأَلْحِقْنِي بِالصَّالِحِينَ ( 83 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 83
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
وَاجْعَل لِّي لِسَانَ صِدْقٍ فِي الْآخِرِينَ ( 84 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 84
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."
وَاجْعَلْنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ النَّعِيمِ ( 85 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 85
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."
وَاغْفِرْ لِأَبِي إِنَّهُ كَانَ مِنَ الضَّالِّينَ ( 86 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 86
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
وَلَا تُخْزِنِي يَوْمَ يُبْعَثُونَ ( 87 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 87
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
يَوْمَ لَا يَنفَعُ مَالٌ وَلَا بَنُونَ ( 88 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 88
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
إِلَّا مَنْ أَتَى اللَّهَ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ ( 89 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 89
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."
وَأُزْلِفَتِ الْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ ( 90 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 90
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَ ( 91 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 91
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ ( 92 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 92
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
مِن دُونِ اللَّهِ هَلْ يَنصُرُونَكُمْ أَوْ يَنتَصِرُونَ ( 93 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 93
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
فَكُبْكِبُوا فِيهَا هُمْ وَالْغَاوُونَ ( 94 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 94
Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.
وَجُنُودُ إِبْلِيسَ أَجْمَعُونَ ( 95 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 95
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
قَالُوا وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَ ( 96 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 96
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
تَاللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَالٍ مُّبِينٍ ( 97 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 97
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
إِذْ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ ( 98 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 98
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
وَمَا أَضَلَّنَا إِلَّا الْمُجْرِمُونَ ( 99 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 99
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
فَمَا لَنَا مِن شَافِعِينَ ( 100 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 100
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٍ ( 101 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 101
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةً فَنَكُونَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ ( 102 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 102
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ( 103 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 103
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 104 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 104
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَتْ قَوْمُ نُوحٍ الْمُرْسَلِينَ ( 105 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 105
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ ( 106 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 106
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ ( 107 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 107
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ ( 108 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 108
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ ( 109 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 109
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ ( 110 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 110
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
قَالُوا أَنُؤْمِنُ لَكَ وَاتَّبَعَكَ الْأَرْذَلُونَ ( 111 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 111
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
قَالَ وَمَا عِلْمِي بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ ( 112 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 112
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
إِنْ حِسَابُهُمْ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّي ۖ لَوْ تَشْعُرُونَ ( 113 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 113
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."
وَمَا أَنَا بِطَارِدِ الْمُؤْمِنِينَ ( 114 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 114
"Ban zama mai kõre mũminai ba."
إِنْ أَنَا إِلَّا نَذِيرٌ مُّبِينٌ ( 115 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 115
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."
قَالُوا لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَا نُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمَرْجُومِينَ ( 116 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 116
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِي كَذَّبُونِ ( 117 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 117
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
فَافْتَحْ بَيْنِي وَبَيْنَهُمْ فَتْحًا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ ( 118 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 118
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
فَأَنجَيْنَاهُ وَمَن مَّعَهُ فِي الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ ( 119 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 119
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ الْبَاقِينَ ( 120 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 120
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ( 121 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 121
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 122 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 122
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
كَذَّبَتْ عَادٌ الْمُرْسَلِينَ ( 123 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 123
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ ( 124 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 124
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ ( 125 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 125
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ ( 126 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 126
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ ( 127 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 127
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."
أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ آيَةً تَعْبَثُونَ ( 128 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 128
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَ ( 129 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 129
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"
وَإِذَا بَطَشْتُم بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَ ( 130 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 130
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ ( 131 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 131
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَاتَّقُوا الَّذِي أَمَدَّكُم بِمَا تَعْلَمُونَ ( 132 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 132
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."
أَمَدَّكُم بِأَنْعَامٍ وَبَنِينَ ( 133 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 133
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
وَجَنَّاتٍ وَعُيُونٍ ( 134 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 134
"Da gõnaki da marẽmari."
إِنِّي أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ ( 135 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 135
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."
قَالُوا سَوَاءٌ عَلَيْنَا أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُن مِّنَ الْوَاعِظِينَ ( 136 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 136
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."
إِنْ هَٰذَا إِلَّا خُلُقُ الْأَوَّلِينَ ( 137 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 137
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko."
وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ ( 138 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 138
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
فَكَذَّبُوهُ فَأَهْلَكْنَاهُمْ ۗ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ( 139 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 139
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 140 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 140
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَتْ ثَمُودُ الْمُرْسَلِينَ ( 141 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 141
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ صَالِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ ( 142 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 142
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ ( 143 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 143
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ ( 144 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 144
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ ( 145 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 145
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."
أَتُتْرَكُونَ فِي مَا هَاهُنَا آمِنِينَ ( 146 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 146
"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ ( 147 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 147
"A cikin gõnaki da marẽmari."
وَزُرُوعٍ وَنَخْلٍ طَلْعُهَا هَضِيمٌ ( 148 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 148
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"
وَتَنْحِتُونَ مِنَ الْجِبَالِ بُيُوتًا فَارِهِينَ ( 149 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 149
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ ( 150 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 150
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَلَا تُطِيعُوا أَمْرَ الْمُسْرِفِينَ ( 151 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 151
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."
الَّذِينَ يُفْسِدُونَ فِي الْأَرْضِ وَلَا يُصْلِحُونَ ( 152 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 152
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."
قَالُوا إِنَّمَا أَنتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَ ( 153 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 153
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."
مَا أَنتَ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا فَأْتِ بِآيَةٍ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ ( 154 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 154
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
قَالَ هَٰذِهِ نَاقَةٌ لَّهَا شِرْبٌ وَلَكُمْ شِرْبُ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ ( 155 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 155
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوءٍ فَيَأْخُذَكُمْ عَذَابُ يَوْمٍ عَظِيمٍ ( 156 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 156
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."
فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا نَادِمِينَ ( 157 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 157
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
فَأَخَذَهُمُ الْعَذَابُ ۗ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ( 158 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 158
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 159 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 159
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ الْمُرْسَلِينَ ( 160 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 160
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ ( 161 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 161
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ ( 162 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 162
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ ( 163 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 163
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ ( 164 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 164
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
أَتَأْتُونَ الذُّكْرَانَ مِنَ الْعَالَمِينَ ( 165 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 165
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"
وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمْ رَبُّكُم مِّنْ أَزْوَاجِكُم ۚ بَلْ أَنتُمْ قَوْمٌ عَادُونَ ( 166 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 166
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"
قَالُوا لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَا لُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمُخْرَجِينَ ( 167 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 167
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ الْقَالِينَ ( 168 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 168
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
رَبِّ نَجِّنِي وَأَهْلِي مِمَّا يَعْمَلُونَ ( 169 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 169
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
فَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَ ( 170 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 170
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
إِلَّا عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَ ( 171 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 171
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.
ثُمَّ دَمَّرْنَا الْآخَرِينَ ( 172 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 172
Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.
وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِم مَّطَرًا ۖ فَسَاءَ مَطَرُ الْمُنذَرِينَ ( 173 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 173
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ( 174 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 174
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 175 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 175
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَ أَصْحَابُ الْأَيْكَةِ الْمُرْسَلِينَ ( 176 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 176
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ شُعَيْبٌ أَلَا تَتَّقُونَ ( 177 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 177
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ ( 178 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 178
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِ ( 179 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 179
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ ( 180 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 180
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
أَوْفُوا الْكَيْلَ وَلَا تَكُونُوا مِنَ الْمُخْسِرِينَ ( 181 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 181
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."
وَزِنُوا بِالْقِسْطَاسِ الْمُسْتَقِيمِ ( 182 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 182
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."
وَلَا تَبْخَسُوا النَّاسَ أَشْيَاءَهُمْ وَلَا تَعْثَوْا فِي الْأَرْضِ مُفْسِدِينَ ( 183 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 183
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."
وَاتَّقُوا الَّذِي خَلَقَكُمْ وَالْجِبِلَّةَ الْأَوَّلِينَ ( 184 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 184
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
قَالُوا إِنَّمَا أَنتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَ ( 185 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 185
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."
وَمَا أَنتَ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ الْكَاذِبِينَ ( 186 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 186
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."
فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفًا مِّنَ السَّمَاءِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ ( 187 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 187
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."
قَالَ رَبِّي أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَ ( 188 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 188
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ الظُّلَّةِ ۚ إِنَّهُ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ ( 189 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 189
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ( 190 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 190
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 191 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 191
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
وَإِنَّهُ لَتَنزِيلُ رَبِّ الْعَالَمِينَ ( 192 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 192
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
نَزَلَ بِهِ الرُّوحُ الْأَمِينُ ( 193 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 193
Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.
عَلَىٰ قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ الْمُنذِرِينَ ( 194 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 194
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.
بِلِسَانٍ عَرَبِيٍّ مُّبِينٍ ( 195 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 195
Da harshe na Larabci mai bayãni.
وَإِنَّهُ لَفِي زُبُرِ الْأَوَّلِينَ ( 196 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 196
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
أَوَلَمْ يَكُن لَّهُمْ آيَةً أَن يَعْلَمَهُ عُلَمَاءُ بَنِي إِسْرَائِيلَ ( 197 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 197
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?
وَلَوْ نَزَّلْنَاهُ عَلَىٰ بَعْضِ الْأَعْجَمِينَ ( 198 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 198
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,
فَقَرَأَهُ عَلَيْهِم مَّا كَانُوا بِهِ مُؤْمِنِينَ ( 199 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 199
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.
كَذَٰلِكَ سَلَكْنَاهُ فِي قُلُوبِ الْمُجْرِمِينَ ( 200 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 200
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
لَا يُؤْمِنُونَ بِهِ حَتَّىٰ يَرَوُا الْعَذَابَ الْأَلِيمَ ( 201 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 201
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.
فَيَأْتِيَهُم بَغْتَةً وَهُمْ لَا يَشْعُرُونَ ( 202 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 202
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
فَيَقُولُوا هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَ ( 203 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 203
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ ( 204 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 204
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?
أَفَرَأَيْتَ إِن مَّتَّعْنَاهُمْ سِنِينَ ( 205 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 205
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
ثُمَّ جَاءَهُم مَّا كَانُوا يُوعَدُونَ ( 206 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 206
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
مَا أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا يُمَتَّعُونَ ( 207 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 207
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.
وَمَا أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ ( 208 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 208
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.
ذِكْرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَالِمِينَ ( 209 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 209
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
وَمَا تَنَزَّلَتْ بِهِ الشَّيَاطِينُ ( 210 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 210
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
وَمَا يَنبَغِي لَهُمْ وَمَا يَسْتَطِيعُونَ ( 211 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 211
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
إِنَّهُمْ عَنِ السَّمْعِ لَمَعْزُولُونَ ( 212 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 212
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
فَلَا تَدْعُ مَعَ اللَّهِ إِلَٰهًا آخَرَ فَتَكُونَ مِنَ الْمُعَذَّبِينَ ( 213 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 213
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
وَأَنذِرْ عَشِيرَتَكَ الْأَقْرَبِينَ ( 214 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 214
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
وَاخْفِضْ جَنَاحَكَ لِمَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ ( 215 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 215
Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
فَإِنْ عَصَوْكَ فَقُلْ إِنِّي بَرِيءٌ مِّمَّا تَعْمَلُونَ ( 216 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 216
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
وَتَوَكَّلْ عَلَى الْعَزِيزِ الرَّحِيمِ ( 217 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 217
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
الَّذِي يَرَاكَ حِينَ تَقُومُ ( 218 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 218
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ ( 219 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 219
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
إِنَّهُ هُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ ( 220 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 220
Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani.
هَلْ أُنَبِّئُكُمْ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ الشَّيَاطِينُ ( 221 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 221
Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٍ ( 222 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 222
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.
يُلْقُونَ السَّمْعَ وَأَكْثَرُهُمْ كَاذِبُونَ ( 223 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 223
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
وَالشُّعَرَاءُ يَتَّبِعُهُمُ الْغَاوُونَ ( 224 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 224
Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.
أَلَمْ تَرَ أَنَّهُمْ فِي كُلِّ وَادٍ يَهِيمُونَ ( 225 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 225
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
وَأَنَّهُمْ يَقُولُونَ مَا لَا يَفْعَلُونَ ( 226 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 226
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?
إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَذَكَرُوا اللَّهَ كَثِيرًا وَانتَصَرُوا مِن بَعْدِ مَا ظُلِمُوا ۗ وَسَيَعْلَمُ الَّذِينَ ظَلَمُوا أَيَّ مُنقَلَبٍ يَنقَلِبُونَ ( 227 ) Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya 227
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email

Select language

Select surah